Connect with us

News

Rikicin gwamnatoci masu adawa a Libya ya kashe mutum 32

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rikici tsakanin ƙungiyoyin da ke biyayya ga gwamnatocin Libya biyu ya yi sanadiyyar kashe mutum 32, a cewar ma’aikatar lafiya ranar Lahadi, sakamakon faɗan da ya ɓarke a baya-bayan nan.

 

Advertisement

Gungun ‘yan bindiga sun yi ta ɓarin wuta da ya lalata asibitoci da dama da kuma ƙona gine-gine tun daga ranar Juma’a da yamma, wanda shi ne mafi muni a birnin Tripoli tun bayan yarjejeniyar tsagaita wuta a 2020.

Pogba na fuskantar ‘kwace da barazana’ daga wata kungiyar masu laifi

Advertisement

Ƙura ta ɗan lafa ya zuwa Asabar da dare, a cewar wakilin kamfanin labarai na AFP.

 

Advertisement

Faɗan ya ɓarke ne bayan cecekuce tsakanin magoya bayan Abdulhamid Dbeibah da na Fathi Bashagha da ke jagorancin gwamnatoci daban-daban kuma suke neman iko da yankunan ƙasar da ke arewacin Afirka.

 

Advertisement

Gwamnatin Dbeibah da aka kafa a Tripoli a matsayin wani ɓangare na yunƙurin zaman lafiya ƙarƙashin shirin Majalisar Ɗinkin Duniya, ta hana Bashagha shiga ofis a can tana mai cewa dole sai an gudanar da zaɓe.

 

Advertisement

Tun bayan kashe Muammar Gaddafi a 2011, Libya ba ta sake samun cikakkiyar gwamnati ba, inda tashin hankali ya fi zaman lafiya yawa.

 

Advertisement

. BBC NEWS

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending