Connect with us

News

Ɗan Shekara 18 ya rasu a ruwa yayin ceto saniyarsa a Jigawa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

Wani matashi ɗan shekara 18, mai suna Adamu Musa, mazaunin Unguwar Magina, a cikin garin Buji da ke Ƙaramar Hukumar Buji a jihar Jigawa, ya rasa ransa a wani tafki a lokacin da ya ke ƙoƙarin ceto saniyarsa da ta zame ta faɗa a lokacin da ya ke kiwo a yankin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar tsaron farar hula, NSCDC, reshen jihar Jigawa, CSC Adamu Shehu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi.

 

An dakatar da ‘yar tseren Najeriya Nwokocha daga wasanni kan amfani da haramtattun ƙwayoyi

Ya ce lamarin ya faru ne a jiya Asabar, da misalin karfe 02:00 na rana, lokacin da matashin ya kaɗa shanunsa guda biyu zuwa gona, ya kuma bar su su yi kiwo a kusa.

Advertisement

Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin shanun sai ta zame ta faɗa cikin ruwan da ke kusa da gonar da su ke kiwon.

PRO ɗin ya ƙara da cewa, a lokacin da saniyar ta faɗa, sai Adamu ya yi maza ga bita cikin ruwan domin ya ceto ta, amma sai ya nutse a ciki.

Shehu ya ce duk ƙoƙarin da mutanen yankin da jami’an NSCDC suka yi na ceto shi, ba a sami gawarsa ba sai karfe 01:00 na safiyar Lahadi.

“An kai gawar asibiti, inda a ka bincika ta sosai aka tabbatar da mutuwarsa, sannan aka mika wa iyayensa domin su yi musu jana’iza yadda ya kamata, inda ita kuma saniyar a ka ce to ta da ran ta,” in ji Shehu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending