Connect with us

News

EFCC ta gurfanar da kakakin majalisar dokokin jihar Ogun a gaban kotu

Published

on

EFCC

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Hukumar da ke yaki da cin hanci da karbar rashawa ta Najeriya EFCC ta gurfanar da kakakin majalisar dokokin jihar Ogun Olakunle Oluomo a gaban wata babbar kotun tarayya da ke jihar Legas, bisa laifin sama da fadi na kudi sama da naira biliyan 2.5

Masu garkuwa da mutane sun bukaci kudin fansa domin sakin matafiya a Ondo

Gidan talabijin na Channels Tv a Najeriya ya ruwaito cewa an gurfanar da kakakin tare da daraktan kudi na majalisar dokokin jihar Oladayo Samuel, da kuma Akawun majalisar Adeyemo Taiwo.

 

Advertisement

Ana yi musu tuhuma 11 da suka hadar da hadin baki, da satar kudi da bayar da bayanan bogi, zargin da dukkansu suka musanta.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending