Connect with us

Entertainment

Wasu Daga Cikin Jaruman Da Aka Cire Yayin Da Aka Shafe Fuskokin Wasu A Cikin Shirin Labarina

Published

on

DAGA KHADIJA ABDULLAH MUHMD

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wasu Daga Cikin Jaruman Da Aka Cire Yayin Da Aka Shafe Fuskokin Wasu A Cikin Shirin Labarina

Advertisement

 

1-Ibrahim Mandawari

Advertisement

Tun da farko Jarumi Ibrahim Mandawari ne aka fara yin waje da shi a cikin shirin LABARINA mai dogon zango, idan baku manta ba shine ya fara fitowa a matsayin Mahaifin Presidor, kafin daga bisani aka cire shi aka sauya da Jarumi Tijjani Faraga, kuma har yau babu cikakken dalili.

2-Nuhu Abdullahi

Advertisement

Nuhu Abdullahi wanda aka aka fi sani da Mahmoud a cikin shirin, shine na biyu a cikin Wanda aka cire a cikin shirin na LABARINA, Rahotanni sun tabbatar da cewar matsala aka samu hakan ta saka dole aka lauya alkalami aka ce Mahmoud ya Mutu ba don ana so ba.

3-Lailah

Advertisement

Maryam Waziri, ita ce ta uku data fita a cikin shirin LABARINA sakamakon Aure data yi a Jihar Kaduna, sai dai kwata kwata labarin bai sake bi ta wajen ta ba bare a iya ganewa ko zaa iya sauya ta da wata, kuma har yanzu masu shirya shirin basa amsa tambaya a kan haka.

4-Nafisa Abdullahi

Advertisement

Nafisa Abdullahi, wacce aka fi sani da Sumayya a cikin shirin, wanda ita ce tauraruwa mai haske, sai da aka kusa yin Uwa-Uban ka da ita kafin ta rubuta takardar yin Murabus, an danganta cire kanta data yi a cikin shirin da samun wata hatsaniya da Nazir Sarkin waka, wasu hujjojin Kuma sun bayyana cewar kan batun bayar da kudin aiki ne sarkin waka yayi mata ba daidai ba a saboda haka aka yi baran-baran.

5-Halima Atete.

Advertisement

Tun bayan da aka fara haska sabon Shirin baa sake ganin Halima Atete a cikin shirin ba har ma ake tunanin an sauya ta da wata Jaruma Mai suna Hajara Mai wushirya, tana nan a cikin shirin.

6-Garzali Miko

Advertisement

Garzali Miko wanda aka fi sani da Habu, a cikin shirin an dauki dogon lokaci baa sake ganin shi a cikin shirin ba, kuma an tabbatar da cewar baza a sake ganin shi a cikin shirin ba.

7-Mai Kemis.

Advertisement

Dambaza’u, ya fito a cikin shirin wanda sune taurarin farko-farko a cikin shirin na LABARINA amma sauya akalar rubutun shirin ya saka dole aka goge babin su.

8-Malam Aminu Saira.

Advertisement

Daraktan Shirin Malam Aminu Saira, shima yana daga cikin jaruman farko-farko a cikin shirin, idan baku manta ba shine ya fara fitowa a matsayin direban Baban Presidor, a farkon Shirin Ibrahim Mandawari ne Baban Presidor kafin daga bisani aka sauya da Tijjani Faraga.

9-Dija

Advertisement

Hafsat Idris, wacce ake yiwa lakabi da Barauniya, tayi shura a cikin shirin kuma ana kiran ta da Dija, salon rubutun labarin ya saka dole aka shafe fuskar ta a cikin shirin ba don ana so ba.

Sauye-sauyen da aka sami a cikin shirin ya saka wasu na ganin cewar yanzu shirin bashi da alkibila, yayi da wasu suke cewar yanzu ne ma Shirin yake daukar seti.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending