Connect with us

News

NULGE Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kin Amincewar Da Majalissa Tayi Na Cin Gashin Kan LGA

Published

on


DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Najeriya (NULGE) reshen jihar Kaduna ta bayyana rashin jin dadin ta dangane da kin amincewa da kudirin dokar cin gashin kan kananan hukumomi da majalisar dokokin jihar Kaduna ta yi.

NULGE ta ce kin amincewa da kudirin ya zama koma baya ga ingantacciyar ci gaban jihar da ma kasa baki daya.

Advertisement

DA ƊUMI-ƊUMI: Dalibai sun tare filin jirgin sama na Legas bisa zanga-zangar yajin aikin ASUU

Majalisar dokokin jihar ta yi la’akari da kudurin a kwanan baya tare da wasu kudirorin da suka samu daga majalisar dokokin kasar amma suka gaza yin aiki yayin da aka zartar da wasu kudirori da dama da suka hada da na ‘yancin cin gashin kai na bangaren shari’a da majalisar dokokin jihar.

Advertisement

A wata sanarwa da shugaban kungiyar NULGE reshen jihar Kaduna, Rayyanu Isyaku Turunku ya fitar a jiya, ya bayyana matakin da majalisar ta dauka a matsayin babban abin takaici domin ya saba wa alkawuran da kungiyar ta dauka.

Ya kara da cewa majalisar zartarwar kungiyar ta kasa za ta sake duba lamarin a lokacin da ya dace sannan ta tashi tsaye.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending