Wani sabon rahoto ya ce ƙananan yara fiye da miliyan goma ne a ƙasashen Gabashin Afirka ke fama da rashin abinci mai gina jiki kuma fiye da 300,000 suna cikin hatsarin mutuwa sanadin yunwa.
Nazarin wanda ƙungiyar ƙasashen yankin IGAD ta ƙaddamar ya yi gargaɗin cewa matsalar rashin abinci za ta ta’azzara, idan ba a samu ruwan sama ba tsawon shekara biyar ke nan a jere.
WAEC ta ƙaryata rahoton cewa ta na ɗaukar ma’aikata
Babban daraktan ƙungiyar, Workneh Gebeyehu ya ƙara da cewa rikici a faɗin yankin ya kawo cikas ga harkar samar da abinci, lamarin da ya ta’azzara wannan matsala.
Ya kuma buƙaci taimakon ƙasashen duniya yayin da yankin Gabashin Afirka ke fama da fari mafi tsayi a cikin shekara 40, wanda shi ne na huɗu a cikin shekara goma
