News
Ɗan takarar majalisar wakilai, Abdulmumin Kofa ya karɓi mutane 2,000 zuwa NNPP
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ɗan takarar kujerar majalisar wakilai ta mazaɓar Kananan Hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya karɓi mutane sama da 2,000 da su ka sauya sheƙa daga jam’iyyu daban-daban a yankin nasa.
Kofa ya karɓe su ne a jiya Litinin a taron ƙaddamar da fara yaƙin neman zaɓen sa, wanda a ka yi a garin na Kofa.
Najeriya ta hana amfani da maganin tarin da ‘ya kashe’ yara a Gambia
Taron ya samu halartar dubban magoya baya daga Kananan Hukumomin Kiru da Bebeji.
Yayin taron, waɗanda su ka koma jam’iyyar NNPP ɗin sun yi alakwarin aiki tukuru wajen baiwa dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar, Rabiu Musa Kwankwaso kuri’a miliyan 5 da kuma ganin jam’iyyar tayi nasara tun daga sama har kasa.
A yayin taron, Kofa ya yi alkawarin idan ya ci zaɓe, zai ci gaba da kawo ayyukan ci gaba kamar yadda ya saba a mazaɓar ta sa.
Taron ya samu halartar ƴan takarar majalissar jiha na Kiru Hon Abubakar Usman Rabula Dana Bebeji Hon Ali Muhammed Tiga da dai sauran yan jam’iyya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
