News
Limaman Kaduna za su gana da ƴan takaran gwamnan jihar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Majalisar malamai da limaman addinin musulunci a jihar Kaduna ta ce za ta gana da ƴan takarar gwamnan jihar domin fahimtar manufar kowane daga cikin su.
Mataimakin shugaban majalisar, Imam Musa Tanimu ne ya bayyana haka ranar Laraba, lokacin da ya gana da manema labaru a jihar ta Kaduna.
Ya ce tattaunawar za ta samar wa al’ummar musulmin jihar alƙibla domin ganin sun zaɓi shugabanni masu gaskiya.
A tattaunawarsa da BBC, Imam Tanimu ya ce sun aika da saƙon gayyata ga ƴan takaran gwamna na jam’iyyu biyar domin halartar tattaunawar, wadda za a yi a ranar Asabar 19 ga watan Nuwamba.
Sai dai ya bayyana cewa malaman ba su da aniyar bayyana goyon baya ga kowane ɗan takara.
Ya buƙaci ƴan takaran da su halarci tattaunawar domin fayyace manufofinsu ga al’umma.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
