Connect with us

News

Limaman Kaduna za su gana da ƴan takaran gwamnan jihar

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Majalisar malamai da limaman addinin musulunci a jihar Kaduna ta ce za ta gana da ƴan takarar gwamnan jihar domin fahimtar manufar kowane daga cikin su.

 

Advertisement

Mataimakin shugaban majalisar, Imam Musa Tanimu ne ya bayyana haka ranar Laraba, lokacin da ya gana da manema labaru a jihar ta Kaduna.

India tayi ragin kudin zuwa aikin hajjin:2023

Ya ce tattaunawar za ta samar wa al’ummar musulmin jihar alƙibla domin ganin sun zaɓi shugabanni masu gaskiya.

Advertisement

 

A tattaunawarsa da BBC, Imam Tanimu ya ce sun aika da saƙon gayyata ga ƴan takaran gwamna na jam’iyyu biyar domin halartar tattaunawar, wadda za a yi a ranar Asabar 19 ga watan Nuwamba.

Advertisement

 

Sai dai ya bayyana cewa malaman ba su da aniyar bayyana goyon baya ga kowane ɗan takara.

Advertisement

 

Ya buƙaci ƴan takaran da su halarci tattaunawar domin fayyace manufofinsu ga al’umma.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending