News
Limaman Kaduna za su gana da ƴan takaran gwamnan jihar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Majalisar malamai da limaman addinin musulunci a jihar Kaduna ta ce za ta gana da ƴan takarar gwamnan jihar domin fahimtar manufar kowane daga cikin su.
Mataimakin shugaban majalisar, Imam Musa Tanimu ne ya bayyana haka ranar Laraba, lokacin da ya gana da manema labaru a jihar ta Kaduna.
Ya ce tattaunawar za ta samar wa al’ummar musulmin jihar alƙibla domin ganin sun zaɓi shugabanni masu gaskiya.
A tattaunawarsa da BBC, Imam Tanimu ya ce sun aika da saƙon gayyata ga ƴan takaran gwamna na jam’iyyu biyar domin halartar tattaunawar, wadda za a yi a ranar Asabar 19 ga watan Nuwamba.
Sai dai ya bayyana cewa malaman ba su da aniyar bayyana goyon baya ga kowane ɗan takara.
Ya buƙaci ƴan takaran da su halarci tattaunawar domin fayyace manufofinsu ga al’umma.
