News
Tinubu ya gana da ƙungiyar kiristoci ta CAN
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ɗan takaran shugaban ƙasa na jam’iyyar All Progressive Congress, Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da zargin cewar ba ya martaba addinin kirista.
Zaɓen da Bola Tinubu ya yi wa tsohon gwamnan jihar Borno sanata Kashim Shettima ya janyo muhawara mai zafi a Najeriyar, kasancewar dukkaninsu mabiyan addinin musulunci ne.
Wasu na ganin hakan tamkar rashin adalci ne ga sauran mabiya addinai a ƙasar mai mutane masu addinai da yare daban-daban.
A wata ganawa da ya yi da shugabannin ƙungiyar ta CAN ranar Laraba, ya ce zaɓen da ya yi wa Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa ba ya da alaƙa da addini.
Ya ce “na zaɓi Shettima ne saboda ina tunanin wanda zai taimaka min wajen tafiyar da mulki.”
Ya ƙara da cewa “ban ce babu mutumin kirki mabiyin addinin kirista da zan iya ɗauka a matsayin mataimaki ba, amma abin da muke buƙata a yanzu shi ne samun mafita ga matsalolinmu.”
Bbc ta rawaito cewa Ya kuma soki waɗanda ke yi masa kallon mai tsattsauran ra’ayin addini.
