Connect with us

News

Tinubu ya gana da ƙungiyar kiristoci ta CAN

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Ɗan takaran shugaban ƙasa na jam’iyyar All Progressive Congress, Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da zargin cewar ba ya martaba addinin kirista.

 

Advertisement

Zaɓen da Bola Tinubu ya yi wa tsohon gwamnan jihar Borno sanata Kashim Shettima ya janyo muhawara mai zafi a Najeriyar, kasancewar dukkaninsu mabiyan addinin musulunci ne.

Limaman Kaduna za su gana da ƴan takaran gwamnan jihar

Wasu na ganin hakan tamkar rashin adalci ne ga sauran mabiya addinai a ƙasar mai mutane masu addinai da yare daban-daban.

Advertisement

 

A wata ganawa da ya yi da shugabannin ƙungiyar ta CAN ranar Laraba, ya ce zaɓen da ya yi wa Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa ba ya da alaƙa da addini.

Advertisement

 

Ya ce “na zaɓi Shettima ne saboda ina tunanin wanda zai taimaka min wajen tafiyar da mulki.”

Advertisement

 

Ya ƙara da cewa “ban ce babu mutumin kirki mabiyin addinin kirista da zan iya ɗauka a matsayin mataimaki ba, amma abin da muke buƙata a yanzu shi ne samun mafita ga matsalolinmu.”

Advertisement

 

Bbc ta rawaito cewa Ya kuma soki waɗanda ke yi masa kallon mai tsattsauran ra’ayin addini.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending