Connect with us

Politics

Jagaba Tinubu ya ziyarci Birnin-Gwari kafin fara yakin neman zabensa a Kaduna

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Jagaba Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci Birnin-Gwari kafin fara yakin neman zabensa a Kaduna

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da tawagarsa sun isa jihar Kaduna inda za su gudanar da yakin neman zabensa a jihar ta Kaduna a ranar Talata.

Advertisement

Likitocin Da Suka Samu Horo A Kasashen Waje 439 Sun Fadi Jarabawar Gwaji

Tinubun ya samu rakiyar abokin takararsa Sanata Kashim Shettima da babban daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Filato, Simon Lalong da gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, da na Kebbi, Atiku Bagudu sai kuma na Jigawa, Abubakar Badaru.

Gwamna Nasir El-Rufai da dan takarar gwamna na jam’iyyar APC na jihar, Sanata Uba Sani da wasu manyan jami’an gwamnatin jihar Kaduna ne suka tarbe su a filin jirgin saman Dana dake Kaduna.

Advertisement

 

Bayan isowarsa jihar ta Kaduna, tsohon gwamnan na jihar Legas ya zarce jaje zuwa karamar hukumar Birnin Gwari, daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan tada kayar baya da ‘yan fashin daji suka addaba don ya gane wa idanunsa halin da yankin yake ciki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending