Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Umurci EFCC Ta Bude Asusun Bankin Gwamnatin Jihar Osun Da Ta Kulle 

Published

on

Tinubu Bola 750x430

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umurci Hukumar EFCC da ta gaggauta komawa kotu domin janye umarnin da ta samu na dakatar da asusun gwamnatin jihar Osun.

Advertisements
Advertisements

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Tinubu ya ce ko da yake bai saba tsoma baki cikin ayyukan hukumomin yaki da cin hanci ba, ya damu da lokacin da aka bijiro da matakin ba, kasancewar jihar Osun na gab da gudanar da zaben gwamna.

Advertisements

KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli

Advertisements
Advertisements

Shugaban ya ce bai san da matakin EFCC tun da farko ba, amma ya yi gargadin cewa bai kamata a dauki wani mataki da zai iya haifar da zargin cewa gwamnatin tarayya na kokarin yin tasiri kan zaben ba.

Saboda haka, ya ce ya umurci EFCC da ta janye umarnin kotun tare da dakatar da duk wani mataki da ta dauka kan gwamnatin jihar Osun domin kare mutuncin tsarin dimokuradiyya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending