News
Muna Da Ikon Dakatar Da Asusun Gwamnatin Jiha Har Na Tsawon Sa’o’i 72 Kafin Umarnin Kotu — EFCC
Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arziki zagon ƙasa (EFCC) ta ce matakin da ta dauka na dakatar da asusun Gwamnatin Jihar Osun ya yi daidai da tanadin doka.
Daraktan hulda da Jama’a na hukumar, Wilson Uwujaren,ya bayyana cewa an dauki matakin ne bayan gano wasu mu’amala da ya tada zargi a asusun cikin makon da ya gabata, kuma ba sai an samu umarnin kotu ba kafin yin hakan.
Wasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Motar Yan KAROTA A Kano
Ya ce dakatarwar ta shafi asusu guda daya kacal ne, ba wai an daskarar da dukkan asusun Gwamnatin Jihar Osun ba ne,kamar yadda wasu ke ikirari.
Uwujaren ya kara da cewa an gano ana tura makudan kudade daga asusun zuwa wasu kamfanoni da dama, lamarin da ya sa EFCC ta dauki mataki domin kare kudaden gwamnati da hana yiwuwar karkatar da su.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News2 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
