Connect with us

News

Muna Da Ikon Dakatar Da Asusun Gwamnatin Jiha Har Na Tsawon Sa’o’i 72 Kafin Umarnin Kotu — EFCC

Published

on

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arziki zagon ƙasa (EFCC) ta ce matakin da ta dauka na dakatar da asusun Gwamnatin Jihar Osun ya yi daidai da tanadin doka.

Daraktan hulda da Jama’a na hukumar, Wilson Uwujaren,ya bayyana cewa an dauki matakin ne bayan gano wasu mu’amala da ya tada zargi a asusun cikin makon da ya gabata, kuma ba sai an samu umarnin kotu ba kafin yin hakan.

Wasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Motar Yan KAROTA A Kano

Ya ce dakatarwar ta shafi asusu guda daya kacal ne, ba wai an daskarar da dukkan asusun Gwamnatin Jihar Osun ba ne,kamar yadda wasu ke ikirari.

Uwujaren ya kara da cewa an gano ana tura makudan kudade daga asusun zuwa wasu kamfanoni da dama, lamarin da ya sa EFCC ta dauki mataki domin kare kudaden gwamnati da hana yiwuwar karkatar da su.

 

Advertisement

PUNCH

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending