Connect with us

News

MDD ta yi kira da a kai dauki ga fasinjojin jirgin ruwan da suka makale a tekun Andaman su 150

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira ga kasashen da ke kusa da tekun Andaman ta su kai dauki ga wani jirgin ruwa da ya dauko mutane akalla ‘yan gudun hijirar Rohingya 150 daga Myanmar.

 

Advertisement

Jirgin ya kasance babu wutar lantarki a cikinsa tsawon makonni uku.

DA ƊUMI-ƊUMI: Argentina ta lashe gasar cin Kofin Duniya

Mutanen da ke cikin jirgin da aka samu ji ta bakinsu ta wayar tauraron dan adam, sun ce basu da ruwa da abinci.

Advertisement

 

Fasinjojin cikin jirgin sun hadar da mata da yara, kuma akwai rahotannin da ke cewa akwai wadanda suka mutu a cikinsu.

Advertisement

 

Rahotanni sun ce ‘yan gudun hijirar Rohingya sun bar sansanonin da suke zaune a kudancin Bangladesh sun nufi Malaysia.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending