News
DSS ta janye jami’anta daga tawagar Gwamna kan rashin jituwa da ‘yan sanda
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS) ta janye dakarunta da ta tura gadin Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke da gidan Gwamnatin Jihar da kuma Ofishin Gwamnan.
Jita-jita dai ta yi kamari cewa hukumar ya yanke shawarar daukar matakin ne bayan Gwamnan ya zage ta.
MDD ta yi kira da a kai dauki ga fasinjojin jirgin ruwan da suka makale a tekun Andaman su 150
To sai dai mai magana da yawun Gwamnan, Olawale Rasheed, a cikin wata sanarwa ya ce janyewar na da nasaba ne da ‘kishin’ da ake samu tsakanin jami’an ’yan sanda da na DSS din da aka tura su yi gadin Gwamnan.
Rasheed ya ce matakin lamari ne da ya shafi hukumomin ’yan sanda da na DSS, ba Gwamnan ba.
Sanarwar ta ce, “Muna so mu bayyana cewa an sami wata ’yar rashin fahimta tsakanin jami’an ’yan sanda da na DSS.
“Tuni an kai rahoton zuwa ga hedkwatocin hukumomin tsaron biyu da lamarin ya shafa kuma za su magance ta.
“Muna tabbatar wa jama’a cewa babu wani abun tayar da hankali. Gwamnanku na cikin aminci, kuma harkokin mulki na ci gaba da gudana yadda ya kamata,” inji sanarwar.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
