Connect with us

Sports

Martinez Ya Zama Sabon Kocin Portugal

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

Tsohon mai horas da tawagar ’yan wasan kasar Belgium, Roberto Martinez, ya zama sabon kocin kasar Portugal.

Advertisement

 

Martinez ya maye gurbin Fernando Santos wanda Hukumar Kwallon Kafar kasar Portugal ta sallama bayan rashin nasara a hannun Maroko a matakin Kwata-Fainal a Gasar Kofin Duniya da aka gudanar a Qatar a 2022.

Advertisement

Dalilin Da Rikicin Zabe Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa A Najeriya

 

Kocin, dan asalin kasar Sifaniya, ya samu kalubale a Gasar Kofin Duniya, inda Belgium ta gaza fitowa daga Matakin Rukuni, lamarin da ya sanya ya yi murabus daga matsayinsa.

Advertisement

 

Belgium ta fito a rukuni daya da Kanada, Maroko da kuma Croatia amma ta gaza yin katabus.

Advertisement

 

 

Advertisement

Babban kalubalen Martinez a yanzu shi ne kai Portugal ga nasara a Gasar Nahiyar Turai da za a yi a 2024 a Kasar Jamus.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending