News
Ɗalibin jami’a ya rataye kansa a Ondo
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wani ɗalibin jami’ar Fasaha ta tarayya da ke Akure a jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya ya rataye kansa a ɗakinsa.
Rahotonni sun ce ɗalibin na aji uku a jami’ar inda yake karantar fannin fasahar zane-zanen kayayyaki.
Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Bullar Cutar Diphtheria A Kananan Hukumomi 13.
Jaridar Punch a Najeriya ta ambato wata majiya na cewa abokan marigayin ne suka fara gano gawarsa, bayan da suke je ɗakin suka tarar da shi a kulle, suka yi magana suka ji shiru daga nan suka yanke shawarar karya ƙofar, inda suka same shi a rataye ya mutu.
Mai magana da yawun run dunar ‘yan sandan jihar Misis Funmilayo Odunlami ta tabbatar da faruwar lamarin.
Ta ƙara da cewa tuni aka kai gawar ɗakin ajiye gawarwaki tare da kuma ƙaddamar da bincike domin gano abin da ya janyo ɗalibin ya rataye kansa.
-
News1 day ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News4 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
