Sports
Arsenal na ci gaba da jan ragamar teburin Firimiyar Ingila yayin duke Manchester United
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta doke Manchester United da ci 3 da 2 a wasan hamayya da suka buga a filin wasa na Emirates da ke Landan.
Dan wasan gaban Manchester United, Marcus Rashford ne ya fara zura kwallo a minti 17, amma a minti na 23 dan wasan gaban Arsenal, Nkeitah ya farke kwallon.
PDP ta zargi Tinubu da yin safarar miyagun kwayoyi zuwa kasashen waje.
Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci Bukayo Saka ya saka Arsenal a gaba, inda ya zura mata kwallo ta biyu a minti na 53, sai dai Martinez ya sake farke wa Manchester kwallon a minti na 59.
An kai ruwa rana a wasan inda Arsenal ta dinga kai munanan hare-hare kafin daga bisani dan wasanta, Nkeitah ya sake zura kwallo a minti 90, kwallon da ta raba gardama a wasan.
A halin yanzu dai Arsenal na ci gaba da jan ragama a teburin Firimiyar Ingila da maki 50 cikin wasanni 19 da ta buga, yayin da Manchester City ke biye mata a baya da maki 45 a wasanni 20.
