News
Breaking news: INEC ta kara wa’adin karbar katunan zabe
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta kara wa’adin karbar katunan zabe na dindindin (PVCs) zuwa ranar 5 ga Fabrairu, 2023.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta tsayar da ranar 31 ga watan Janairu a matsayin wa’adin tattara katinan zabe amma kwamishinan zabe na kasa Festus Okoye ya ce an kara wa’adin ne domin baiwa ‘yan Najeriya karin lokacin karbar katinan su.
Channel
Advertisements
