News
Rundunar Yan sanda sun kama mutum 27 kan zargin tashin hankali a Shagamu
Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya ta kama wasu mutane 27 da ake zargi da hannu cikin wani tashin hankali da ya ɓarke a garin Shagamu a ranar Litinin.
Ana zargin masu zanga-zangar da lalata bankuna, sakamakon rashin takardun kuɗi na naira a na’urorin ATM mallakar bankunan.
‘Yan ƙasar dai na kokawa kan ƙarancin sababbin takardun kuɗin,a yayin da gwamnati ta haramta ta haramta amfani da tsofaffin takardun kudi na naira 500 da kuma 1,000.
Advertisements
