News
Za a fara ƙidaya a ranar 3 ga watan Mayu — Gwamnatin Tarayya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Za a fara kidayar jama’a da gidaje na 2023 a ranar 3 ga Mayu, kamar yadda gwamnatin tarayya ta tabbatar.
Garba Abari, mamba ne a kwamitin yada labarai da bayar da shawarwari kan kidayar jama’a da gidaje na kasa na shekarar 2023 ne ya tabbatar da hakan a yau Lahadi a Abuja lokacin da ya bayyana wa dandalin Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasapl.
Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamna
Ya ce atisayen na kwanaki uku zai fara ne daga ranar 3 ga watan Mayu sannan kuma za a kare a ranar 5 ga watan Mayu a fadin kasar.
Mista Abari, wanda shi ne babban daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta kasa, NOA, ya bayyana cewa, aikin kidayar zai kama kowane mutum, gida da kuma tsarin tsare-tsare na kasa da aiwatar da ayyuka.
A cewar sa, an sauya ranar ne saboda dage zaben gwamnoni da na majalisun jihohi da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi a shekarar 2023.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
