News
kasar Amurika Zata Dafawa Tinubu Baya Domin Inganta Tattalin Arziki Da Tsaro
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaban kasar Amurika,Joe Biden ya yi alkawarin yin aiki tare da sabon shugaban kasa, Bola Tinubu ta fannin inganta tattalin arziki da kuma sha’anin tsaro.
Shugaba Joe Biden wanda ya turo tawaga mai karfi daga Amurika domin shaidar bukin rantsar da Tinubu, ya baiyana haka ne ta cikin wata sanarwa, wadda ke taya Tinubun murnar rantsuwar kama aiki da yayi a ranar litinin.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na yin aiki kafada da kafada da Tinubu domin karfafa zumuncin dake tsakanin Amurika da kuma nan Najeriya.
Joe Biden ya ce yana da kwarin gwiwa akan irin ingantattun manufofi dake tsakanin kasashen biyu.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
