Connect with us

News

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLHAI

 

Biyo bayan jita-jitan mutuwar gwamnan Jihar Ondo, Oluwarotimi Akeredolu, a ranar Asabar, Gwamnatin jihar ta bukaci jama’an jihar da su yi watsi da wanan jita-jitar tare da cewa Gwamnan yana raye.

Ana ta samun tashin hankali dai a jihar sakamakon kokonton da jama’a ke yi na cewar ina gwamnan yake tun lokacin da ya dawo dag hutun shekara.

Kungiyar OPEC za ta yi taro don duba yiwuwar rage yawan man da take fitarwa

Babbar jam’iyyar adawa a jihar, PDP ta fito a ranar Asabar din ta bukaci wadanda suka boye gwamnan da su fito su bayyana wa jama’a ina gwamnan yake domin toshe kafar jita-jitan.

A sanarwar manema labarai da jami’an watsa labarai na jam’iyyar a jihar, Kennedy Ikantu Peretei, ya fitar, PDP ta, “Tun bayan da wasu kafafe suka yada labarin da ke cewa Gwamnan ya shiga mayuwacin hali na rashin lafiyar da ba ya iya gudanar da aikinsa, hakan ya jefa jama’a cikin damuwa wanda a ta hakan ne aka yada cewa kila ma ya mutu.

Advertisement

“Gwamnan bai dawo ofis don cigaba da aiki ba tun lokacin da hutunsa na shekara ya kare a watan March. Ko wajen bikin kaddamar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ba a gano Akeredolu ba.

 

 

LEADSHIP

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending