Connect with us

News

Wani mutum dan shekara 35 ya rataye kansa saboda tsadar rayuwa a Jigawa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

 

Advertisement

Wani magidanci mai suna Samaila Ilu mai shekaru 35 ya rataye kansa har lahira sakamakon mawuyacin halin da yake ciki a jihar Jigawa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar wa da jaridar DAILY POST faruwar lamarin.

Advertisement

Mutane 6,000 sun tsere daga muhallinsu sakamakon ambaliyar ruwa a Jihar Neja

A cewarsa, “A ranar 17/08/2023 da misalin karfe 11:00 na safe ‘yan sanda sun samu rahoton cewa wani matashi mai suna Samaila Ilu mai shekaru 35 a kauyen Dungun Tantama a karamar hukumar Hausa ya bar gidansa.

Ya ce daga baya an tsinci gawarsa rataye akan bishiya da igiya, ana zaton ya kashe kansa ne.

Advertisement

Shiisu ya ce, tawagar ‘yan sanda sun kwashe gawar tare da kai shi asibiti domin a duba gawar.

Ya ce tun daga lokacin aka mika shi ga ‘yan uwansa domin yi masa jana’iza.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending