News
Ana Sa Ran Titin Layin Dogo Daga Kano Zuwa Maradi Nanda Shekarar 2025
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ana sa ran kammala aikin titin layin dogo daga Kano zuwa Maradi na Jamhuriyar Nijar da zai lakume dala biliyan biyu da gwamnatin da ta gabata karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta kaddamar, ana sa ran kammala aikin zuwa shekarar 2025.
Da yake jawabi yayin wata ziyarar aiki da yaki wajen aikin da ya faro daga Dawanau a Kano zuwa Jamhuriyar Nijar, Ministan Sufuri, Sanata Saidu Ahmad Alkali, ya bayyana jin dadin yadda ayyukan ke gudana.
Gwamnatin kasar Kongo ta musanta ikirarin juyin mulkin kasar
Ya ce, aikin shimfida fandisho ya kai matakin kammala da kashi 80 cikin 100, kuma za a fara aikin layin dogo na hakika nan ba da dadewa ba.
Dangane da ko dan kwangilar zai cimma burin kammala aikin cikin lokacin daya ambata, ministan ya nuna gamsuwa da kwarin guiwa da yadda aikin ke gudana.
Saidu Alkali ya kuma ya yaba aikin share daji, kuma kwangilar tana tafiya yadda ya kamata ba tare da wata matsala ba. Kazalika, Ministan ya ce akwai bukatar dan kwangilar ya kasance a shirye domin sadaukarwa ga ci gaban kasa a karkashin jagorancin gwamnatin Tinubu.
Wani labarin kuma Gwamnatin kasar Kongo ta musanta ikirarin juyin mulkin kasar
A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.
A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.
Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.
Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
