News
Kotun Kolin ta tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin shugaban kasar.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotun Kolin Nijeriya ta tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin shugaban kasar.
Kotun Kolin ta tabbatar da hakan ne a hukuncin da ya zama na karshe da ta yanke a yau Alhamis a kan zaben shugaban Nijeriya wanda Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na Labour ke kalubalanta.
Tawagar alkalai bakwai ce ta yanke hukuncin bayan yin nazari a kan hukunce-hukuncen da kotunan baya suka yanke.
Tun farko Jaridar Inda Ranka ta rawaito cewa Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP sun nemi Kotun Kolin ta soke zaben Bola Tinubu wanda kotun sauraren kararrakin zabe ta tabbatar da nasararsa a matsayin shugaban kasa a zaben 2023.
Advertisements
