Connect with us

Business

Kamfanin Dangote ya zargi BUA da daukar nauyin yada labaran karya akansa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Katafaren Kamfanin Dangote da ke Najeriya ya musanta zargin cewar ya sanya kansa cikin haramcaciyar musayar kudaden waje, inda ya gargadi masu yada irin wannan zargin cewar ya na yiwa kasa zagon kasa, da su kaucewa yin haka.

Kamfanin ya gabatar da wannan gargadi ne sakamakon wasu rahotannin da aka wallafa a kafofin intanet dake zargin cewar shugaban kwamiti na musamman da shugaban Najeriya ya kafa Jim Obazee domin binciken ayyukan Babban Bankin Najeriya a karkashin jagorancin Godwin Emefiele na gudanar da bincike a kan sa saboda hannu wajen wannan badakalar da kuma halarta kudaden harum.

Advertisement

Ku Guji Manyan Otal A Najeriya, Amurka Ta Gargadi ‘Yan Kasarta

Sanarwar da kamfanin ya gabatar ta ce, Dangote ya bayyana rahotanin a matsayin masu tsauri, yayin da ya zargi abokin adawarsa, wato kamfanin BUA da hannu a ciki dumu dumu.

 

Advertisement

Dangote yace tun daga shekarar 2016 aka fara yada irin wadannan labarai na kanzon kurege a jaridun BusinessDay da Leadership, inda yace sun sake farfado da su ne yanzu domin gabatar da su kamar wasu sabbin labarai.

 

Advertisement

Kamfanin yace abin takaici ne yadda a ranar 14 ga watan Maris na shekarar 2016, Jaridun BusinessDay da Leadership suka wallafa rahotan cewar Kamfanin Dangote ya karkata Dala biliyan 3 na kudaden waje zuwa wasu kamfanoninsa dake wajen Najeriya, matakin dake da nasaba da halarta kudaden haramun.

 

Advertisement

Dangote ya ce wancan rahotan da aka yi a shekarar 2016 shine kuma aka sake wallafa shi a yanzu da sunan wani Ahmed Fahad, a matsayin korafin da aka gabatarwa shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma Jim Obazee, shugaban kwamitin bincike na musamman dake gudanar da bincike a kan ayyukan Babban Bankin Najeriya.

 

Advertisement

Kamfanin ya ce abin takaici shine yadda wasu kafofin intanet suka dinga daukar labarin suna wallafa shi da zummar bata masa suna.

 

Advertisement

Dangote ya ce yunkurin wadanda suka kitsa wannan labari na kawar da hankalin jama’a da kuma farfado da tsohon labarin abin takaici ne, ganin yadda wadancan jaridu guda 2 da suka wallafa shi a shekarar 2016 suka fito fili suka kuma nemi gafarar shugabannin kamfanin Dangoten da kuma janye labaran da suka yi a kai baki daya.

 

Advertisement

Kamfanin ya ce Jaridun BusinessDay da Leadership sun tabbatar da cewar kamfanin BUA ne ya dauki nauyin wallafa rahotanin.

 

Advertisement

Dangote yace yana samo kudaden waje domin gudanar da ayyukan sa ne ta hanyoyin bankuna kamar yadda dokokin CBN suka tanada, kuma suna gabatar da takardun da suka dace wajen samun kudaden sayen kayayyakin aiki da kuma kafa kamfanonin su ciki harda na siminti.

 

Advertisement

Kamfanin ya ce an kuma bayyana karara yadda aka gudanar da hada hadar kudaden da kuma lokacin da za’a biya basussukan da aka karba kamar yadda ka’idodin duniya suka tanada.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending