News
Kungiyar Hamas ta lalata motoci 160 na sojojin Isra’ila
DAGA UASIR SANI ABDULLAHI
Sashen soji na kungiyar Hamas ya ce ya lalata motoci 160 na dakarun Isra’ila tun lokacin da suka kaddamar da hare-hare ta kasa a Gaza, yana mai cewa ya lalata motoci 25 a cikin kwana biyu da suka gabata.
Hakan na faruwa ne a yayin da rundunar sojin Isra’ila ta ce an kashe dakarunta 43 tun da ta kaddamar da kutse ta kasa a Gaza.
A wani labarin kuma Dakarun Isra’ila sun kaddamar da jerin hare-hare ta sama a yankuna daban-daban na Gaza, a cewar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida da Tsaron Kasa ta Gaza.
Ma’aikatar ta fitar da sanarwa da ke bayani dalla-dalla kan jerin hare-hare ta sama da dakarun Isra’ila suka kai a sassa daban-daban na Gaza.
“Jiragen sama na dakarun mamaya sun kaddamar da jerin hare-hare a harabar Mahadar Saraya da ke Birnin Gaza,” in ji ma’aikatar, tana mai karawa da cewa Isra’ila ta kuma “kaddamar da samame a yankin Tal al Zaatar da kuma Asibitin Indonesian Hospital da ke arewacin Gaza.”
Ta kara da cewa jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare a arewaci da tsakiyar Birnin Gaza da yankin Al Nasr da kuma yankunan kusa da garin Jabalia da ke arewacin Gaza.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
