Connect with us

News

Zaben Nijeriya Ya Zama Iya Kudinka Iya Shagalinka -Shehu Sani

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Tsohon dan majalisar tarayya, Sanata Shehu Sani ya ce har sai an gyara tsarin zaben kasar nan domin hana sayen kuri’u,amma idan ba a dauki wani mataki ba Nijeriya zabe a Nijeriya zai zama kamar cin Kasuwa.

Shehu Sani ya bayyana haka ne a wani sako da ya wallafa a shafin sa na X a ranar Lahadi yayin da yake mayar da martani kan rahotannin sayen kuri’u da suka kawo cikas a zaben gwamnoni da aka gudanar ranar Asabar a jihohin Imo, Kogi da Bayelsa.

Advertisement

Gwamna Abba Kabir Yusuf Mai Kishin Harkar kiwon Lafiya ne – Kwamishinan Lafiya 

Jami’an tsaro sun kama wasu ‘yan siyasa a ranar Asabar bayan da aka kama su da makudan kudade, ana zarginsu da sayen kuri’u.

A cewar Shehu Sani, idan kasar ta ci gaba da tafiyar da tsarin dimokuradiyya da ke karfafa sayen kuri’u, masu kudi ne kawai za su ci gaba da mulki.

Advertisement

Sanarwar ta ci gaba da cewa,matukar za mu gudanar da tsarin dimokuradiyya wanda zai karfafa tare da amincewa da yin amfani da kudi wajen siyan kuri’un wakilan jam’iyya da kuma sayen kuri’un al’umma.

To zabe a Nijeriya zai kasance ne kawai ga mutanen da za su iya zuba kudadensu su sayi kuri’u ba tare da wata matsala ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending