News
Gwamnan Kogi Yahaya Bello Ya Rufe Asusun Gwamnatin Jihar
DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA
Gwamnan Kogi Yahaya Bello Ya Rufe Asusun Gwamnatin Jihar
Yanzu haka dai gwamnatin Kogi ta bayar da umarnin garkame dukkan asusun Gwamnatin jihar da na kananan hukumomi ba tare da wani bata lokaci ba.
Harry Maguire ya yafe wa ɗan majalisar Ghana da ya yi masa shaguɓe
Sanarwar da Kwamishinan Kudi, Asiwaju Asiru Idris ya sanya wa hannu, ta ce babu wani zargi ko wani nau’i na biyan kudi daga asusun gwamnatin jihar daga yanzu.
A cewar sanarwar, “An soke duk wani umarni na tsaye da kuma umarnin saka hannun jari nan da nan.
“An kulle dukkan asusun jihar Kogi daga yau Alhamis 22 ga watan Nuwamba 2003.”
A wani labarin kuma Harry Maguire ya yafe wa ɗan majalisar Ghana da ya yi masa shaguɓe
Dan majalisar Iran ya ce ɗaukar hoto ko bidiyon mutane ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar, tare da yinkira ga hukumomi da su fayyace dokar.
Moinuddin Saeedi na mayar da martani ne kan masu ɗaukar bidiyo ko hotunan mutanen da ke sanye da hijabi.
Dan majalisar – wanda ke wakiltar yankin Chabahar ya ƙara da cewa ba a bayyana masu kula da dokar sanya hijabin ga jama’a ba.
“Don haka dole a fayyace waɗanda za su gudanar da aikin, samar da su aka yi, ko kuwa jami’an tsaro ne?, inda ba fayyace ba, to kenan aikin ba shi da inganci.
Labarai da hotunan dakarun da ke kula da masu sanya hijabi, sun yaɗu a shafukan sada zumunta, inda mutane ke ta muhawara a kansu a faɗin ƙasar.
