Connect with us

News

Harin Bama-Bamai Kan Masu Maulidi A Kaduna Ya Fusata ‘Yan Najeriya

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

An shiga rudani da kuma Makoki a ranar Litinin kan harin bam da sojojin Najeriya suka kai a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna a ranar Lahadi, wanda ya yi sanadin mutuwar Mutanen kauyen 85.

Advertisement

Mazauna garuruwan da abin ya shafa sun ce suna gudanar da Maulidi ne, lokacin da sojoji suka jefa bama-baman, al’amarin da ya jawo Allah wadai a cikin gida da waje.

Gwamnatin Tarayya ta ce ta dauki nauyin wakilai 422 ne kawai daga cikin ‘yan Najeriya dubu 1 da 411

Mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Hadiza Balarabe ta ziyarci malaman addinin musulunci a jihar domin kwantar da tarzoma, yayinda yadda gwamnan jihar, Sanata Uba Sani, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan tashin bam din.

Advertisement

Kungiyar Kiristocin Najeriya da Kungiyar matasan Arewa da kungiyar kare hakki ta Human Rights Watch, da Amnesty International, da dai sauransu, sun yi Allah wadai da hare-haren bama-bamai da sojoji kaiwa.

A wani labarin kuma Gwamnatin Tarayya ta ce ta dauki nauyin wakilai 422 ne kawai daga cikin ‘yan Najeriya dubu 1 da 411

Advertisement

Hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Kaduna ta ce aƙalla mutum 85 ne, kawo yanzu, aka tabbatar sun mutu a harin da aka kai jihar.

Ofishin hukumar na Arewa maso yamma ya samu bayanai daga hukumomin yankin cewa tuni aka yi jana’izar mutanen da suka rasu, ana kuma ci gaba da yin bincike.

Advertisement

Tun farko dai rundunar sojin saman ƙasar ta musanta hannu a kai harin.

A jiya Litinin ne, Majalisar Dattawan Najeriya ta lashi takobin gudanar da bincike kan harin kuskuren da rundunar sojin kasar ta kai, da ya janyo asarar rayuka.

Advertisement

Harin dai ya faru ne yayin da mutanen ke tsaka da taron Mauludi da suke yi duk shekara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending