News
Jami’yyar PDP Ta Kalubalanci Gwamnatin Jihar Jigawa Bisa Cire Kudade Ba Bisa Ka’ida Ba
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’yyar PDP a jihar Jigawa da kalubalanci gwamnatin jihar bisa cire kudade daga cikin asusun kananan hukumomi ba bisa ka’ida ba, domin daukar nauyin zaben kananan hukumomi dake tafe shekara mai zuwa.
Amma shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi a jihar Jigawa da hadimin gwamnan jihar sun bayyana wannan zargi a matsayin karya da kaharu.
An Tantance Alkalai 11 Domin Zama Sabbin Alkalan Kotun Kolin Najeriya
Shugaban jami’iyyar PDP na karamar hukumar Kazaure Mustapha Ibrahim Danshatu,ya na zargin gwamnatin Jiha da cire kudaden kananan hukumomi tare da ajiye su a asusun wasu bankuna.
Yayi kira ga shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa Ola Olukoyede da yayi bincike kan zargin karkatar da wannan makudan kudade da gwamnatin Jigawa keyi.
Amma shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi na Jihar Jigawa Bala Usman Chamo yace wannan labari ba gaskiya bane. Shima hadimin gwamnan jihar Jigawa kan ayyukan kananan hukumomi Abdurrahman Alkassim,ya musanta wannan zargin.
A wani labarin kuma An Tantance Alkalai 11 Domin Zama Sabbin Alkalan Kotun Kolin Najeriya
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
