Connect with us

News

Ana Hasashen Gwamnan Kano Zai Koma APC, Murta Sule-Garo Na Iya Zama Mataimakin Gwamna

Published

on

Abba

Rahotanni daga majiyoyi masu kusanci da harkokin siyasar Kano na nuna cewa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, na iya ficewa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC a makon farko na watan Janairun 2026, idan babu wani sauyi a minti na ƙarshe.

Matakin, idan ya tabbata, zai kawo ƙarshen alaƙar siyasa da ta shafe kusan shekaru arba’in tsakanin gwamnan da jagoran NNPP a ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya kasance ubangidansa a siyasa.

Advertisement

Dakarun Soji Sun Kashe ’Yan Bindiga 9 Bayan Sun Yi Artabu Da Su A Kano 

Abba Yusuf shi kaɗai ne gwamna da jam’iyyar NNPP ke da shi a halin yanzu. Saboda haka, ficewarsa za ta sa jam’iyyar ta rasa matsayin jam’iyyar da ke riƙe da kujerar gwamna a Nijeriya.

Shirye-shiryen shiga APC

Advertisement

Majiyoyi sun ce gwamnan ya fara tsara shirin shiga APC ne duba da yadda jam’iyyar ke shirin gudanar da tarukan zaɓen shugabanni a watan Fabrairu. Ana ganin wannan a matsayin wata dama da zai ba shi damar samun cikakken iko da tsarin APC a jihar Kano.

Rahotannin sun ce tun watanni da suka gabata gwamnan ke ƙoƙarin samun goyon bayan ‘yan Majalisar Tarayya, ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano da kuma shugabannin ƙananan hukumomi, domin ƙarfafa matsayinsa a sabuwar jam’iyyar da ake hasashen zai shiga.

Advertisement

Wata majiya ta ce wakilin mazabar Tarauni a Majalisar Wakilai—wanda ke da alaƙar aure da Kwankwaso—shi ne kaɗai aka tabbatar zai ci gaba da kasancewa tare da Kwankwaso, yayin da wakilan Nassarawa, Ungogo da Kumbotso ke ci gaba da yin nazarin yanayin siyasar kafin yanke shawara.

Matsayin ‘yan Majalisar Jiha

Advertisement

Binciken DAILY NIGERIAN ya nuna cewa mafi yawan ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano daga NNPP, ciki har da Kakakin Majalisar Yusuf Falgore, sun amince da shirin gwamnan na barin jam’iyyar. A cewar rahoton, aƙalla ‘yan majalisa 25 daga cikin 27 sun nuna goyon baya, duk da cewa biyu daga cikinsu sun rasu.

Haka kuma, rahotanni sun ce gwamnan ya samu goyon bayan yawancin shugabannin ƙananan hukumomi a jihar, kodayake wasu na ci gaba da nuna biyayya ga Kwankwaso a fili.

Advertisement

Kwankwaso ya kira taron shawara

A yayin da jita-jitar ficewar gwamnan ke ƙara yaɗuwa, Rabiu Kwankwaso ya kira ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kano zuwa wani taro a gidansa da ke Miller Road.

Advertisement

A cewar majiyoyi, Kwankwaso ya bayyana musu cewa alamun siyasa sun nuna gwamnan na shirin barin NNPP, inda ya ce duk wanda ya yanke shawarar bin gwamnan yana da ‘yancin yin hakan.

Ya kuma bayyana damuwarsa, yana mai cewa ba a gabatar masa da hujjar da za ta sa a koma APC ba. An rawaito yana cewa, “Allah ne ya ba mu mulki a 2023; Allah ne kuma zai iya ci gaba da ba mu nasara a 2027.”

Advertisement

A ƙarshen taron, ‘yan majalisar sun amince su nemi ganawa da gwamnan domin tattaunawa ta ƙarshe. Sai dai majiyoyi sun ce gwamnan ya bayyana musu cewa ya riga ya yanke shawarar komawa APC, kuma ba ya ganin yiwuwar sauya matsaya.

Makomar mataimakin gwamna

Advertisement

Rahotanni sun ce mataimakin gwamnan Kano, Aminu Abdulsalam, na iya fuskantar matsin lamba sakamakon wannan sauyin siyasa.

A cewar majiyoyi, ana duba yiwuwar maye gurbinsa da tsohon ɗan takarar mataimakin gwamna na APC a zaɓen 2023, Murtala Sule-Garo, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin daidaita dangantaka da manyan jiga-jigan APC a Kano.

Advertisement

Haka kuma, ana hasashen tsohon ɗan takarar gwamna na APC a 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, zai iya tsayawa takarar Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya a zaɓen 2027.

Rikici da sauyin yanayi a NNPP

Advertisement

Tun bayan hukuncin Kotun Koli kan zaɓen gwamnan Kano, rahotanni sun nuna ƙaruwar rashin jituwa tsakanin Abba Yusuf da Kwankwaso. A watan Nuwamban 2024, DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa gwamnan ya daina halartar tarukan jam’iyyar tare da ƙin amsa kiran wayar Kwankwaso.

A shekarar 2024, taken siyasa na “Abba Tsaya da Kafarka” ya fara yaduwa a Kano, inda wasu ke kira ga gwamnan da ya zama mai cin gashin kansa a harkokin siyasa.

Advertisement

Gwamnan ya taɓa musanta alaƙarsa da wannan yunkuri, yana mai jaddada biyayyarsa ga Kwankwaso.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, kakakin gwamnan Kano, Sanusi Dawakin-Tofa, bai amsa kiran waya ko saƙon da aka aika masa ba domin jin martaninsa kan batun.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending