Connect with us

News

Najeriya Za Ta Tura Jirage Marasa Matuka A Kan Iyakokin Kasar 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS) ta ce za ta fara amfani da jirage masara matuka wajen yin sintiri a kan iyakokin kasar.

Kwamturola-Janar ta hukumar, Caroline Wura-Ola Adepoju, ta ce tuni Gwamnatin Tarayya ta fara tattauna da kamfanin samar da na’uori na Huawei da ke kasar China kan samar da fasahar na’ura wajen sintiri a kan iyakokin Najeriya.

Hukumar INEC ta Rantsar da Sabbin Kwamishinonin Zaben Tara

Ta sanar da haka ne a taron Ranar ’Yan Gudun Hijira ta Duniya a ranar Talata.

Game da fargabar ’yan Najeriya kan yiwuwar harin kuskure irin wanda jirgin soja mara matuki ya kai wa masu taron Mauludi a Kaduna, shugabar hukumar ta ba da tababcin cewa babu wata matsala da za a samu wajen amfani da jirage marasa matuka a kan iyakokin kasar.

Advertisement

Aminiya ta ruwaito cewa ewa za a yi amfani da jirage marasa matuka a kan iyakokin kasar ne kawai wajen tattara bayanai kai-tsaye.

A wani labarin kuma Hukumar INEC ta Rantsar da Sabbin Kwamishinonin Zaben Tara

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending