News
Hukumar INEC ta Rantsar da Sabbin Kwamishinonin Zaben Tara
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaban Hukumar zabe mai zman kanta ta kasa INEC Farfesa Mahmoud yakubu ya rantsar da sabbin shugabannin Hukumar a shelkwatar Hukumar zabe Dake birnin tarayya Abuja
Farfesa Mahmoud yakubu ya rantsar dasu awani taro irinsa na farko tun Bayan kammala zaben Jihohin Kogi-Bayelsa- Da jihar Imo.
Sake Fasalin Kudi Da Gwamnatin Da Ta Shude Tayi Ya Durkusar Da Harkar Manoma A Najeriya
Shugaban kasa Bola Ahmad tunubu shine ya nada shugabannin Guda Tara bayan majalisar dattawan Nigeria ta amince dasu, duk da kalubalantar matakin Hakan Ga wasu kungiyoyin Nigeria sukayi
Ana zargin cewa akwai wasu daga cikin wadanda Shugaban kasar ya nada Yan jam’iyyar APC ne Wanda Hakan ya Saba da doka acewar kungiyoyin
Punch Ta rawaito Cewa Bayan rantsar dasuda Farfesa Mahmoud yakubu yayi Tuni ya turasu jihohin Kebbi, Borno, Edo, Akwa Ibom, Kaduna, Kwara, Ondo, Ekiti, da jihar Nasarawa
A wani labarin kuma Sake Fasalin Kudi Da Gwamnatin Da Ta Shude Tayi Ya Durkusar Da Harkar Manoma A Najeriya
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
