Connect with us

News

Mai ƙwacen waya’ da mota ta buge a jihar Kano ya rasu

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Wani matashi da ake zargi da ƙwace wa wata mata waya a Kano ya rasa ransa sanadiyyar raunukan da ya samu bayan mota ta buge shi a lokacin da yake yunƙurin tserewa.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na facebook, mai magana da yawun ƴan sandan Najeriya a jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce mutumin ya rasu ne a yau Talata a sibitin Murtala da ke Kano.

Advertisement

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 2 Na Jami’ar Al-Qalam

A ranar Litinin rundunar ƴan sandan ta tabbatar da cewa wata mota ta kaɗe wani ɗan ƙwacen waya a titin zoo road da ke Kano.

Bayan haka ne aka garzaya da shi asibiti, inda aka tabbatar cewa ya samu karyewar kashin baya da kuma fashewar kai.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending