News
Bom ya tashi da wasu ‘Almajirai’ masu karatun islamiyya, ɗaya ya rasu, 10 sun ji rauni a Kaduna
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wani bom da ya fashe a kauyen Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna ya yi sanadin mutuwar wani dalibin makarantar Islamiyya yayin da wasu goma suka samu raunuka.
Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Kaduna, Samuel Aruwan, a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, ya ce jami’an tsaro na gudanar da bincike a kan fashewar bom ɗin.
Aruwan ya ce, “A cewar rahotannin farko da aka samu daga kauyen da kuma jami’an tsaro, daya daga cikin daliban da ke karatu a karkashin wani malamin garin ya dauko wani abu daga daji, wanda daga baya ya fashe a tsakanin ‘yan uwansa dalibai.”
Ya ce ya zuwa yanzu an tabbatar da mutuwar almajiri daya mai suna Zaidu Usman, yayin da wasu kimanin 10 suka samu raunuka kuma suna samun kulawa a asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika-Zariya.
Aruwan ya ce, “Gwamna Uba Sani na jihar ya samu rahoton cikin kaduwa da bakin ciki, sannan ya aika sakon ta’aziyya ga wadanda abin ya shafa da iyalansu, inda ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma basu lafiya.”
Ya ce gwamnan ya kuma yi kira ga iyaye da shugabannin al’umma da su kara sanya ido kan ayyukan ‘ya’yansu a koda yaushe domin guje wa irin haka a gaba.
