News
An Samu Bullar Cutar Zazzabin Lassa A Abuja
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
An tabbatar da kamuwar mutum biyu da cutar Zazzabin Lassa a Babban Birnin Tarayya Abuja.
Sakatariyar Hukumar Lafiya ta birnin, Adedolapo Fasawe, ce ta sanar da haka a ranar Litinin, amma ta ce babu wanda cutar ta kashe a birnin.
Abubuwan Da Ke Hana Magance Matsalar Tsaro A Arewacin Najeria – Sharrif
Adedolapo Fasawe ta ce an gano masu dauke da kwayar cutar ce a Babban Asibitin Bwari da kuma Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja.
Cikin wadanda suka kamun har da wani dan watanni 14, wanda cutar ce sanadin rasuwar mahaifiyarsa a Jihar Bauchi, kafin a dawo da shi Abuja.
Advertisements
