Sports
Aljeriya Ta Kori Kocinta Bayan Cire Ta A Gasar Cin Kofin Afrika.
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
A ranar Laraba Aljeriya ta kori kocinta, Djamel Belmadi, bayan da aka fitar da ita daga Gasar Cin Kofin Afrika.
Aljeriya ta dauki wannan mataki a kan Belmadi ne bayan da ta sha kashi a hannun Mauritania a ranar Talata a wasansu na karshe na rukuninsu a Ivory Coast.
Dalilan da suka sanya naki gabatar da shaidar kammala karatu na na Sakandare -Muhammadu Buhari
Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Aljeriya, Walid Sadi, ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Na hadu da kocin kasar Djamel Belmadi don tattauna abubuwan da ke tattare da wannan rashin nasarar, kuma mun cimma yarjejeniyar kawo karshen dangantakarmu da kuma dakatar da kwantiraginsa.”
Korar Belmadi ta zo ne a ranar da Ivory Coast mai masaukin baki ta kawar da kocinta Jean-Louis Gasset a tsakiyar gasar sannan Ghana ta kori Chris Hughton bayan ficewarta.
-
News5 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
