Sports
Aljeriya Ta Kori Kocinta Bayan Cire Ta A Gasar Cin Kofin Afrika.
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
A ranar Laraba Aljeriya ta kori kocinta, Djamel Belmadi, bayan da aka fitar da ita daga Gasar Cin Kofin Afrika.
Aljeriya ta dauki wannan mataki a kan Belmadi ne bayan da ta sha kashi a hannun Mauritania a ranar Talata a wasansu na karshe na rukuninsu a Ivory Coast.
Dalilan da suka sanya naki gabatar da shaidar kammala karatu na na Sakandare -Muhammadu Buhari
Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Aljeriya, Walid Sadi, ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Na hadu da kocin kasar Djamel Belmadi don tattauna abubuwan da ke tattare da wannan rashin nasarar, kuma mun cimma yarjejeniyar kawo karshen dangantakarmu da kuma dakatar da kwantiraginsa.”
Korar Belmadi ta zo ne a ranar da Ivory Coast mai masaukin baki ta kawar da kocinta Jean-Louis Gasset a tsakiyar gasar sannan Ghana ta kori Chris Hughton bayan ficewarta.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
