Connect with us

News

Shugaba Tinubu ya isa Abuja bayan kammala ziyara a Faransa

Published

on

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya isa birnin tarayya, Abuja, bayan kammala ziyara a kasar Faransa

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya isa birnin tarayya, Abuja, bayan kammala ziyara a kasar Faransa domin gudanar da harkokinsa.

Tinubu ya sauka filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da misalin karfe 8:50 na dare inda ya samu tarba daga tawagar gwamnati karkashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume.

Advertisement

Hauhawar farashi ba za ta ragu ba sai Najeriya ta rage kayan da take bukata daga waje’ —Gwamnan CBN 

Haka nan, tawagar takunshi manyan jami’ai irin su Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila; Ministan Abuja, Nyesom Wike da sauransu.

Tun a ranar Laraba ta makon jiya Tinubu ya bar Nijeriya zuwa Faransa, kuma wannan ita ce ziyararsa ta biyu a kasar tun bayan da ya zama Shugaban Kasa a watan Mayun 2023.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending