News
Shugaba Tinubu ya isa Abuja bayan kammala ziyara a Faransa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya isa birnin tarayya, Abuja, bayan kammala ziyara a kasar Faransa domin gudanar da harkokinsa.
Tinubu ya sauka filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da misalin karfe 8:50 na dare inda ya samu tarba daga tawagar gwamnati karkashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume.
Hauhawar farashi ba za ta ragu ba sai Najeriya ta rage kayan da take bukata daga waje’ —Gwamnan CBN
Haka nan, tawagar takunshi manyan jami’ai irin su Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila; Ministan Abuja, Nyesom Wike da sauransu.
Tun a ranar Laraba ta makon jiya Tinubu ya bar Nijeriya zuwa Faransa, kuma wannan ita ce ziyararsa ta biyu a kasar tun bayan da ya zama Shugaban Kasa a watan Mayun 2023.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
