Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Nemi Gwamnonin Jihohi Da Su Yi Watsi Da Sabanin Siyasa Su Hada Kai Wajen Gina Kasa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira ga gwamnonin jihohi da su yi watsi da sabanin siyasa su hada kai da gwamnatin tarayya wajen gina kasa.

Advertisement

Tinubu ya yi wannan kiran ne a lokacin buda baki tare da gwamnoni a fadar gwamnati da ke Abuja, a jiya Alhamis.

Ana Zargin Wani Mutum  Da Kashe Mijin Ƙanwarsa Kan Gishirin N20 A Jihar Kano

Ya kuma jaddada muhimmancin a jiye siyasa a gefe a fuskanci shugabanci, inda ya ce akwai bukatar hadin kai kai a tsakanin masu ruwa da tsaki.

Advertisement

Da yake karin haske kan muhimmancin watan Ramadan Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi amfani da lokutan wajen yin addu’o’i, da kuma sadaka.

Shugaban ya bayyana kwarin guiwar samun mafita mai dorewa a nan gaba, inda ya ce gwamnatin sa na iya bakin kokartinta wajen shawo kalubalen da kasar nan ke fuskanta. Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, Shugaban kungiyar Gwamnonin Najeriya kuma Gwamnan Jihar Kwara, ya yabawa gwamnatin tarayya bisa bayarda umurnin raba hatsi da ya kai tan 42,000.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending