News
Dubun Wani Gardi Ya Cika,An Kama Shi A Ɗakin Kwanan Ɗalibai A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an Civil Defence’ reshen jihar Kano sun Yi nasarar damƙe wani gardi mai suna Muhammad Munzali ɗan garin Ƙaura Gidan Damo a ƙaramar hukumar Shanono.
Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar NSCDC, Ibrahim Abdullahi,shi ne ya tabbatar da kamen a yau Juma’a.
Ya ce Jami’an sun damƙe wanda ake zargin ne da misalin karfe 10 na dare a ranar Laraba a lokacin da yake ƙoƙarin kutsawa cikin ɗakin kwanan ɗaliban na jami’ar Skyline wanda ke kan titin Sardauna Crescent, Nassarawa GRA,Kano
“Wanda ake zargin yayi ɓadda kama da shigar mata inda yayi ƙoƙarin kutsawa ɗakin kwanan ɗaliban,Ko Da aka cafke shi an same shi da layu a jikin sa,” cewar PRO .
A Cewar Ibrahim zuwa yanzu ana cigaba da gudanar da bincike domin gano hujjar sa na yin wannan kutse inda daga nan ne za a san wani mataki za a ɗauka.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
