Connect with us

News

Matsalar intanet a Najeriya da wasu ƙasashe zai iya shafe wata ɗaya ana fama nan gaba – Mainone

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

An sanar da cewa gagarimin aikin gyaran wayoyin kebul na intanet da ke ƙarƙashin ruwan teku, wanda lalacewar su ya kawo matsalar intanet a Najeriya da wasu ƙasashen Afrika, zai iya kai makonni biyar ana faman gyara nan gaba.

Advertisement

Kamfanin MainOne, wanda shi ne ke samar da data wadda ake buɗe intanet da ita ƙasashen Afrika ta Yamma da ƙasashen Kudancin Afrika, shi ne ya bayyana haka a ranar Juma’a.

Kiran Ruwa: Ƙabilu Da Ba Su Ga Maciji Da Juna Sun Kashe Sojoji 16 A Harin Kwanton Ɓauna, Ciki Da Janar, Manjo Da Kaftin

A cikin sanarwar ta ranar Juma’a, MainOne ya kuma yi ƙarin bayani dangane da katsewar da wayoyin kebul ɗin suka yi a ƙarƙashin teku, sai kuma bayanin irin ƙoƙarin gyaran da ake kan yi.

Advertisement

Cikin sanarwar da kamfanin ya bayar a shafin sa na intanet, ya ce: “Wayoyin kebul ɗin intanet na MaiOne da ke ƙarƙashin teku su na kai saƙonni ƙasashen Afrika da dama shi ya sa hakan ta faru.”

Premium Times ta ruwaito cewa MainOne ya ce sun rattaba yarjejeniyar gyara da kamfanin Atlantic Cable Maintenance and Repair Agreement (ACMA), domin ya gyara kebul ɗin can a ƙarƙashin ruwan teku.”

Advertisement

Sanarwar ta ce matakin farko shi ne a samu jirgin da zai yi ninƙaya a ƙarƙashin ruwa, domin ya gano ainihin wayoyin da suka katse, sai kuma gano daidai wuraren da za a yi gyaran.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending