News
Yajin Aiki: Mambobin Ƙungiyar SSANU Da NASU Sun Garƙame Kofar Shiga Jami’ar BUK
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ƙungiyar manyan ma’aikatan Jami’oin Najeriya, SSANU da kuma ta ma’aikatan jami’a da basa koyarwa, NASU reshen jami’ar Bayero da ke Kano sun rufe Ƙofar shiga jami’ar a yajin aikin gargaɗi na kwana bakwai da suka soma.
Ma’aikatan na buƙatar Gwamnatin tarayya ta cika musu alƙawuran da ta yi musu.
Majalisar Wakilai Ta Amince Da Naira Tiriliyan 1.28 Kasafin Kuɗin Abuja
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ɗalibai ke jarrabawar a jami’ar lamarin da hana su samun shiga makarantar.
Wikki Time ta ruwaito cewa SSANU da NASU sun shiga yajin aikin na gargaɗi na kwana bakwai ne domin neman gwamnati ta biya musu wasu haƙƙoƙinsu.
Ciki har da rashin biyan albashinsu na wata 4 da gwamnatin ƙasar ba ta yi ba na lokacin da suka shiga yajin aiki na ƙasa baki ɗaya, a shekarar 2022.
Ƙungiyoyin sun nuna rashin jin daɗinsu kan rashin biyan mambobinsu albashin duk kuwa da cewa gwamnatin tarayya ta biya takwarorinsu na malaman jami’oi nasu kuɗaɗen.
-
News6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
