Connect with us

News

Mutum Huɗu Sun Rasa Ransu A Tirmitsitsin Karɓar Zakka A Jihar Bauchi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Akalla mutane hudu ne suka rasa rayukansu a wani turmutsitsi a ƙoƙarin su na karɓar Zakka da ɗan kasuwa AYM Shafa ya bayar a rabawa mabuƙata a jihar.

Advertisement

Wikkitimes ta tattaro cewa turmutsitsin ya faru ne a yau Lahadi a yayin da matan da ke wurin ke ƙoƙarin tilastawa kansu shiga ciki sakamakon haka ne yawancinsu suka fadi kasa aka tattake su, wanda hakan yayi asarar rayukan mutane huɗu.

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

Tuni dai aka garzaya da su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) Bauchi domin kula da lafiyar waɗanda suka jikkata.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending