News
Mutum Huɗu Sun Rasa Ransu A Tirmitsitsin Karɓar Zakka A Jihar Bauchi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Akalla mutane hudu ne suka rasa rayukansu a wani turmutsitsi a ƙoƙarin su na karɓar Zakka da ɗan kasuwa AYM Shafa ya bayar a rabawa mabuƙata a jihar.
Wikkitimes ta tattaro cewa turmutsitsin ya faru ne a yau Lahadi a yayin da matan da ke wurin ke ƙoƙarin tilastawa kansu shiga ciki sakamakon haka ne yawancinsu suka fadi kasa aka tattake su, wanda hakan yayi asarar rayukan mutane huɗu.
Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji
Tuni dai aka garzaya da su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) Bauchi domin kula da lafiyar waɗanda suka jikkata.
Advertisements
