News
DA ƊUMI-ƊUMI: Kotu ta yanke wa dan China da ya kashe budurwarsa ƴar Kano hukuncin kisa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wata babbar kotu a jihar Kano ta yanke wa Geng Quandong, ɗan ƙasar China da ya kashe budurwarsa Ummukulsum Buhari hukuncin rataya.
Kotun ta samu Quandong da laifin kisan Ummukulsum, wacce aka fi sani da Ummita, laifin da ya saɓawa sashi na 221 na kundin dokokin laifuka na jihar Kano.
Wannan dalili ne ya sanya kotun ta yanke wa Quandong, mai shekaru 47 hukuncin kisa.
A tuna cewa a ranar 16 ga watan Satumbar 2022 ne Quandong ya caccaka wa budurwar tasa Ummita wuka har ta ce ga garinku nan a gidan su da ke unguwar Jambulo a Kano.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
