News
Akalla Mutane 200 Ne Suka Mutu Sakamakon Tsananin Zafi a Adamawa
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Akalla mutane 200 ne suka mutu sakamakon tsananin zafi da aka fuskanta daga ranar 1 zuwa 13 ga watan Mayu a Yola, babban birnin jihar Adamawa.
Mazauna yankin da suka zanta da wakilin jaridar Daily Trust sun koka kan yadda yanayin zafi ya yi kamari
Wanda hakan yake kimanin digiri 47 zuwa 50, wanda masana suka bayyana a matsayin matakin hadari, inda suka ce hakan na iya haifar da tsananin zafi .
Ɓangaren Shari’a Ita Ce Babbar Matsalar Mu a Ƙasar Nan Ba INEC Ba- Peter Obi
Bayanan da ba a hukumance ba a cibiyar makabartar Yola (YCC) da ke yankin Damare a babban birnin jihar, sun ce adadin wadanda suka mutu sakamakon tsananin zafi da ba a saba gani ba daga ranar 1 zuwa 13 ga Mayu, 2024 ya kai 400.
Advertisements
