News
Gwamnatin Shugaba Tinubu Ce Silar Rugujewar Najeriya -Babachir Lawal
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Engr Babachir Lawal, ya ce tun daga ranar 29 ga watan Mayu da aka rantsar da Bola Ahmad Tinubu Najeriya ta rasa Seti ta koma tudu da gangare .
Sakataren ya ƙara da cewa sanarwar janye tallafin man fetur da Tinubu ya yi a ranar da aka rantsar da shi ya jefa kasar cikin mawuyacin taɓarbarewar tattalin arziki.
Haka kuma Ya ce sanarwar cire tallafin man fetur ya yi sanadiyyar haifar da karuwar kuɗaɗen sufuri kasancewar itace ƙofar duk wata kasuwanci a Najeriya.
Advertisements
