Connect with us

Sports

Manchester City Ta Lashe Gasar Firimiyar Kasar Ingila Karo Na 10 A Tarihi

Published

on

DAGA UMMAR IBRAHIM HOTORO 

Manchester city tayi nasarar doke kungiyar kwallon kafa ta westham da 3-1 a babban filin wasanta na Al-Ittihad ta hannun dan wasa phill poden wanda ya zura kwalleye 2 tare da kwallo guda daga dan wasa Rodri.

Advertisement

Kungiyar ta manchester city tana da jumilar maki 91 wadda tafi kowace kungiya yawan maki sae Arsenal mai fatan lashe kofin wadda ta kare a matsayin ta 2 a gasar ta wannan shekerar.

Shugaban Kasar  Iran Ebrahim Raisi ya yi hatsarin jirgin sama

Itama kungiyar kwallon kafa ta Arsenal tayi nasara akan Everton da ci 2-1 amma duk da hakan hakansu bai cimma ruwa ba domin dai sun gaza lashe gasar da suke ta kokarin dauka.

Advertisement

Yanzu haka kungiyar ta manchester city tana da jumular kofunan firimiyar ta kasar Ingila guda 10 chif- chif, wanda hakan ka iya zama dama wajen shafe tarihin wasu kungiyoyin, musamman manyan kungiyoyin da aka dade ana fafatawa dasu.

Manchester city tayi rashin nasara a wasan kofin zakarun nahiyar turai akan kungiyar kwallon kafa ta Real madrid a bugun daga kai sai mai tsaron raga, amma yanzu a iya cewa kwalliya tabiya kudun sabulu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending