Connect with us

News

Ranar Tarin Fuka: Gwamnan Jihar Kano ta kammala shirye-shirye don gudanar da gwaji da kuma bayar da magani kyauta

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin Jihar Kano ta ce ta kammala shirye-shirye don gudanar da gwaji da kuma bayar da maganin cutar tarin fuka kyauta a jihar Kano na aƙalla yara 6,000

Kwamishinan Lafiyar Jihar Kano Dr Abubakar Labaran Yusuf ne ya baiyyana hakan ranar Litinin a Kano, hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake tunawa da ranar yaki da cutar tarin fuka ta duniya.

Kotuna guda biyu sun ba da umarni daban-daban kan korar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na biyu

Kamar yadda aka saba duk shekara, ranar 25 ga watan Maris, ita ce ranar da duniya ke tunawa da kuma sabunta yaki da cutar mai hadarin gaske.

Dr Labaran ya ce gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf ta kammala shirye-shirye don gudanar da gwaji da kuma bayar da maganin cutar tarin fuka kyauta a jihar Kano.

Ya yi kira ga duk mazauna jihar da su kai kansu a duba su idan suna fama da tari har na tsawon makonni biyu ko fiye, inda ya ce gwamnatin jihar ta samar da wani shiri na yi mazauna jihar gwaji da bayar da magungunan cutar kyauta.

Advertisement

Haka zakika Dr Labaran wanda ya yaba da kokarin da kungiyoyi masu bayar da tallafi ke yi wajen yaki da cutar tarin fuka da sauran cututtuka a jihar.

Dr Labaran ya ce a shekarar 2023, jihar ta samu akalla mutum 114 da aka gano aka yi musu magani a jihar Kano kuma babu wani yaro da ya mutu sakamakon cutar tarin fuka.

Kazalika, ya jaddada kudirin ma’aikatar na hada hannu da hukumomi masu bayar da tallafi don kawo karshen cutar tarin fuka a jihar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending